Advertisements

IMG 20220121 WA0314

WATA FITSARA PAGE 28

Posted by

WATA FITSARA PAGE 28

 

Advertisements

WATA FITSARA

     By
Fadeela Lamido

                            Page 28

Advertisements

Dariya Sa’ed da Galadima sukayi yayin da Ahmad ya yamutsa fuska kuna wasa dani”

         ********

Misalin 10:12pm Samha ta koma gidan Hajjah, lokacin ta cire rai da dawowar su daga ita har driver dan haka tasha Mamaki sosai data ganta”

Advertisements

       A’a Kun dawo?, Danaga dare yayi saina dauka sai gobe zaki dawo”

    Cikin rashi. Kwarin jiki tace a’a”

     Toh yaya? yabaki kudin kuwa??

   Eh Hajjah yabada nakirata tabada acct number ta ya tura Mata”

      Yauwa aikinga haka yafi ko?

    Hade fuska tayi kamar tace wayyo Allah Hajjah Amman waishi zai amso da kansa, sannan Wai bazanje duk ranar ba Wai kwana biyu ko uku kawai zanje, kuma waishi zaikaini cikin awa daya yamaido ni

       Dariya Hajjah tayi sannan tace”

      Rabo dashi, neman mgn yake, kibishi duk a yadda yaso”

       Matso hawaye tayi kuma beban kudi ba”

    Aina gaya miki neman mgn yake, yana sane sarai da abun da yake yi, nina baki kudin ko ba shikenan ba”

     Dadi taji sannan ta saki ranta tunani ta shigayi agidan Abbanta koda yaushe tana cikin kudi, Amman Uncle Ahmad yanzun yabar yi Mata yadda yake Mata ada”

          *********

Ranar da zasu fara bikin da safe tunani yamata yawa, Bata tunanin an dinka kayan sannan akwai abubuwa da yawa da take son saya wadda zai cikasa kwalliyar tata duk da cewa tasan tana Sabbin kaya cikin lefen da Uncle Ahmad yakai gidan su, Amman gaba daya bata da burin saka su, suna ma can gidan Ahmad Bata taba ganin irin su ba”

         Tana daga kwance saman gadonta taji Muryan Ahmad daga idonta tayi ta kalli agogo 11:30am cikin sauri ta diro ganin babu shi afalon yasa jikinta yayi sanyi dakin hajjah ta nufa da nufin yin korafi turus tayi ganin Ahmad zaune daf da Hajjah mgn yake cikin wani irin yanayi kamar me Shirin yin kuka yayin da Hajjah ke bubbuga bayansa Dagowa sukayi suka kalleta gaba daya cikin sauri Ahmad ya gyara Fuskansa yayin da yabi Samha da kallo”

     Zama tayi tana fadin”

    Cab di bakaga gidan yai maka wani iri ba kafa dade bakazo ba🤔

   Hmmm aikece wani irin, Hajjah ko murmushi kawai tayi sannan ta shiga duba kanyan dake gabanta”

      Fitowa take dasu daya bayan daya tana fadin Masha Allah murmushi Fatima tayi ganin har an dinka kayan cikin dinki mekyau, sosai abun ya burgeta”

      Kallon kayan tayi sannan ta mike taje gaban hajjjaah sosai ta nuna murnan ta akan kayan yayin da Ahmad yaita kallon yadda take farin ciki”

     Daya ledan Hajjah ta jawo takalma ne ciki dasu gyale da wasu ‘yan abuwan da ba’a rasaba kayan shafa turare, daga can idonta ya fada kan kwalin waya, sakin kayan tayi ta koma kanta, budewa tayi tare dayin Karan farin ciki, daga Ahmad har Hajjah dariya suke ganin inda take farinci ayanzun Bata kayan take ba, ta wayar take, Dagowa tayi ta kalle Ahmad da Hajjah yadda suke murmushi mikewa tayi da wayar ahannunta sannan ta ajeye a inda ta tashi tare da tsalleke sauran ledojin data baza tsale tayi zuwa jikin Ahmad yayin da babu zato babu tsammani yaji tafado jikinsa, tare da sunbatan fuskan sa baso daya ba ba sau biyu ba agurare daban daban, ganin Hajjah na gurin wata irin kunya wadda be zaton yana da itaba ta mamaye shi saidai har yanzun fuskansa na dauke da murmushi”

     Ganin Bata da niyyar barin gurin ya rike fuskanta da hannun sa guda biyu sannan ya kureta da ido na tsayon wani lokaci, dagata yayi daga cikinsa ya maidata gefensa cikin yanayi irin na wadda ya daburce har yanzun yana Jin inda bakin ta ya sassauka akan kumatun sa”

     Kantawa tayi akirjin sa yayin da tace Uncle nagode”

   Shiko gogan kasa mgn yayi Banda murmushi babu abun da yake sannan ya kasa kallon gefen da Hajjah take, wani irin kunya lokaci daya ta dirar masa”

     Jin taushin ahnnun Fatima yaji cikin hannunsa tana yamutsaahi cikin nata, kamawa yayi ahankali ya shiga yin irin abun da takeyi din danasa hannun, ahankali suka shiga muntsuka hannun juna yayin da kan Samha ke kwance akirjin sa, tunawa da yayi Hajjah na gurin yasashi yai saurin zame hannunsa tare da Satan kallon gurin da take, wayam yagani, ko yaushe ta fita🤔

     Hannun Fatima yakamo tare da leken fuskanta yace”

       Baki da kunya ko??

     Mena yi??

     Kinsa Hajjah ta gudu tabar mu”

     Uncle murnace ta kamani, nagode nagode kaji”

     Kawar da kansa yayi, ai kin riga kin gode Fatima yadda kika min yau ya wanke min zuciyata, nafi bukatar irin wannan godiyar ta aikace bata fada da baki ba, yanzon sai me kuma kike so”

      Jimmm tayi zuwa can tace”

      Kabarni in wuni agidan bikin”

    Jimmm yayi zuwa can yace”

     Shikenan amman yau kawai, saime kuma kike so”

      Cikin murmushi tace ni ko hakama ka burgeni Uncle”

        Murmushi yayi tare da Kara yamutsa hannunta yace”

     Kudi fah? nasan zaki bukata ko??

    Shiru tayi cikin yanayi najin kunya, mikewa yayi tare da ita sannan yace sa hannun ki a aljihuna ki diba inga hankalin ki”

    Murmushi tayi sannan ta nuke kagada”

    Bazaki diba ba”

   Kaita daga alamar eh sannan ta Kara da cewa hakama na gode sosai”

   Murmushi yayi sannan yasa hannun ya fito da kudi ya mika mata”

   Cikin Jin kunya sosai ta amsa, dagewa domin ta kamo tsayon sa, ta sake sunbatan kan lebensa akaro na biyu yayin da wannan karon batai aune ba taji ya zura harcensa cikin bakin ta, ahankali yake sarrafa harcensa cikin kwarewa da birgewa wannan karon Samha batai kokarin hanawa ba illama wani bakon yanayi daya sameta, batai aune ba ta tsinci kanta da maida martani, haka shima Ahmad ji yayi kamar kafarsa tana kokarin gazawa domin betaba shiga cikin irin yanayin daya shiga  yau ba, sosai yake sauke numfarfashi, yayin da suka kasa barin juna, Jin da yayi kafarsa ta gaza sosai yajawota zuwa gadon Hajjah har yanzun bakinsu na cikin na juna”

     Kasa hanawa tayi tana jinsa yasaka hannunsa cikin rigarta yana me murza kefen cikinta ahankali yana sama da hannunsa”

      Lalubeta yake, yayin da take Kara rikecewa, shi kansa ya fita daga hayyacinsa”

        Sosai Takejin dadin dan haka ta kasa hanawa tanajinsa ya balle zip din rikarta yana yadda yake so da ita, mikewa yayi batare da yana ganin gabansa ba ya isa kofar ya juya key sannan ya dawo ya cire rigar farar shaddar dake jikin sa ya aje agefe, bude ido Fatima tayi ganin yana kokarin kwance zariyar wadonsa yasata saurin Dagowa agodon tana kokarin sauka”

    Barin abun da yake yayi ya karasa ya riketa Ina zaki??

     Cikin sunkuyar dakai tace”

     Dakina zanje”

    Lumshe ido yayi tare da lashe lebe yace”

       Dan bari indan taba jikin ki mana”

     Batare data kalleshi ba tace a’a aika taba……

    Be isheni ba Fatima, barin indan kara kadan”

       Nidai a’a tafiya ta fara yayin data isa kofar tana kokarin bude kofar take fadin kaga ka lalata min zip din rigata ko😔

      Gadon Hajjah ya isa ya kwanta rufda ciki yayin da yake fadin zo in gyara miki”

     Ficewa tayi tana fadin, ba’a so”

        Lumshe ido yayi bayan ya tabbatar da tatafi tabarshi ahaka”

       Ya dade kwance agadon tsayon minti 30 sannan bacci ya dauke shi”

       Hajjah kuwa tunda taga wucewan Samha take jiran na Ahmad amman shi Dan haka yanzun dataga an kwashe tsayon awa daya ta mike ta shiga dakin”

     Sosai abun ya Bata Mamaki ganinsa kwance akan gadon sa yana bacci, rabon dataga haka ta manta, kuma babu riga ajikinsa, haka yavata daman gani farar fatansa data jima Bata gani va, danshi va mutum vane me zama haka ko dakinsa ka shi da wuya ka same shi ahaka”

       Falo ta koma bayan ta tabbatar bacci yake”

Itako Fatima anata bangaren sosai ta shiga wani yanayi da Bata iya misaltashi, toilet ta shiga ta wanke jikinta sannan ta dawo ta kwanta lamo saidai duk da haka batabar Jin abun da takeji akasan taba, runtse idonta tayi sosai take son yanayin yabarta tare dajin haushin kanta dahar tabari ya tabata”

    Kwance tayi ta kasa komai yayin data dau tsayon wani lokaci yanayin yaki barinta

   Jin Kiran sallah ta tabbatar da lallai rana yayi yakamata ta shirya”

    Tashi tayi zaune saidai kafafuwanta ji take basa iya daukanta tsintan kanta tayi da zubar da hawaye tana zaune har 1:30 adaidai lokacin Hajjah ta shiga kwala Mata Kira amsawa tayi yayin da Hajjah tace ki fito ga Ahmad din ya dawo daukan ki”

    To kawai tace sannan tacigaba da zama”

     Hannunta taita sakawa tana cire hawayen da ita kadai tasan suna fitowa”

    Ganin Ahmad kawai tayi ya shigo dan haka ta Kara taburcewa”

    Rasas ta gansa tsaye gabanta kamar shine Ongo lafiya meya same ki???

     Kanta ta dukar sannan ta mike tanufi toilet’

     Dakata malama, dan tsayawa tayi yayin da yai saurin cewa meke damun ki”

    Batare da ta hada idonsa dashi ba tace, kaina ne ke min ciwo”

    Kallonta yayi sosai sannan yace, sannu, in bazaki iya zuwa ba kiyi zamanki kisha magani sai gobe”

    Cikin sauri tace yamin sauki”

     Wanka ta shiga yayin da yabar dakin, tana fitowa ta samu kayanta akan gado gaba daya, bayan tagama shiryawa tsaf ta Sanya kayanta, kamar an gwadata haka tagani cas ta fesa turare sannan ta zare mayafinta daga cikin kayan daya sawo mata ta Sanya Babban ne sosai tunawa tayi da kayan lefen dayakai gidan Hajjah tana ji ana cewa babu gyale, duk hijjabai ne, afili tace wata kila ya canza ra’ayin sa ne, ficewa tayi bayan ta Sanya mayafinta”

     Tunda ta dososa yake kallon ta ya kasa dauke idonsa akanta, Hajjah ce keta yaba kwalliyar yayin da Ahmad yaita murmushi, tare suka fita tana gaba yana binta abaya yayin da yake kare Mata kallo har tanajin hakan ajikinta”

      Koda suka shiga motar suka zauna kin tadata yayi sai kallo yake binta dashi tdarguwa tayi ta dago tace Uncle ka bari”

    Yamutsa fuska yayi yace Meye kuma?

   Kallona kake”

    Ai Nima kallo na kike”

    Wlh ban kalleka ba”

   Idan baki kalleni ba dawani idon kikasan Ina kallon ki?

      Sai yanzun ta dago ta kalleshi cikin ido tace ajikina naji”

     Lumshe ido yayi sannan yace zan iya yadda da haka, me domin ni shaidane  nasani, eh jikin ki naji”

    Me yake ji??

   Komai, ya fada sannan ya dauki hanya”

     Dauke kanta tayi cikin tunani barkatai azuciyanta”

    Misalin Uku saura suka isa gidan su Zainab, sauka tayi sannan yace”

    Karfe nawa zanzo na dauke ki??”

    Uncle idan nagama zan Kira ka……

   Bazan yadda da haka ba”

    Jimmm tayi sannan tace karfe 7…..

Yayi yawa”

    Shiru tayi toh kafada da kanka”

     Zan dawo 5 na dauke ki kizama cikin shiri”

    Shikenan, tafada tare da juyawa, Saida ya tabbatar ta shiga gidan sannan ya wuce”

     Koda ta shiga hiran Uncle dinta tasamo kawayenta nayi yayin da suke yaba halinsa kyansa uwa uba mutunci da Wasa da dariya”

    Sororo tayi sannan tace tace”

   Meke damun ku”

   Labarin Uncle dinki take bamu dayazo karban kayan ki dazon, yana da kirki sosai mutunci ga Wasa da dariya”

    Cafdi, Uncle din??, Wlh baya wani Wasa da dariya nikadai nake ganin wasan sa sai kuma Ummata”

      Kai amma gaskiya nidai ya sakar min fuska sosai, gashi wani Dan mekyau dashi”

    Kin damu wani me kyau ko kina ciki ne??

   Cewan Samha data tsare wata kawar su Hassana da ido”

      Ai wlh da zaice yana Sona dana soshi Dan Ina son kyakyawan mutum saidai wannan Uncle din naki nasan yana da Mata ko??

    A’a, bashi da mata tikeken  gauro ne nan da kika ganshi , adadin shekaruna adadin shekarun da akayi ana kala masa gauro”

     Dariya suka kwashe dashi gaba daya yayin da Aisha tace ke kiji tsoron Allah Fatima, kina nufin Kusan 18 ya isa aure amman biyi ba har yau to me yake jira??

    Oho masa bazai wuce yawon bididi ba,  kika sani ko yana ‘yan harkokin sa, hakanan zai zauna ne yaki aure”

    Gaba daya suka hada baki wajen cewa wannan daganin sa salihine shikenan kuma dan beyi aure ba sai zargi?

    Eh mana, tsoho ne sa’an Mamana ne fah, koni yanzun ahaka aure nake so bare Kuma shi”

    Sowa sukayi cikin darrarraku Aisha tace”

  Ni wlh gani nake ma Uncle din naki kamar son ki yake wani lokacin sainaga kamar yanai miki kallon soyayya, ke kanki wani lokacin abun dai naku akwai alamar tambaya”

    Ni bawani abu tsakanin mu, dacen dai naso shi kadan lokacin bani da wayau yanzun ko nayi wayau ba abun da zanci dashi”

      Kina nan ai zakiga matarsa, ai irin su basa kwantai yana da kyau fah”

    Cikin kawar dakai Samha tace kima Sha kurumin ki yana da budurwa koma matarsa ce wayasani, ranar nan dayakaini Office dinsu naji yana Kiran wata Sweet heart”

    Wasu daga ciki ne sukace kedai Fatima da alama haushin uncle dinan naki kike ji bakya fadan alheri akan sa

   Toh nidai ya isheni kumabar min zancen sa Dan Allah”

     Runtse Ido tayi yayin da take Jin zainab na fayyacewa sauran kawayen dangantar dake tsakanin Ahmad da Samha, yayin da dayawa daga ciki sukace a alallai zai iya aurenta”

     Gani basu da niyar bari ta mike ta gyara mayafinta ta fice agidan gaba daya”

      Mashin kawai ta tare tahau unguwar su Khadija ta fada masa, suna tafe tanajin haushin su Aisha sukama zance daya sunki bari, daman can ita yau tunda Uncle ya tabata bajin dadi jikinta take ba”

Inna yalwa ce tafara ganin ta, oyoyo tashiga Mata yayin da ta saki fara’a ahankali take gaida kowa sannan ta nufi dakin Inna wato mahaifiyar Khadija”

     Kwance ta hangi Khadija yayin da Khadija tai saurin zabura dalilin Jin kamshin turaren Ahmad datayi zubawa kofa Ido tayi Samha ce kadai tsaye”

  Inna ta gaidar sannan ta zauna suna gaisawa da Inna”

    Bayanta amsa tace daga Ina kike ko Ahmad din ne ya kawo ki??

   A’a Inna nikadai nazo”

   Toh Ina Ahmad din kidai kwace manashi tunda akayi bikinan inajin sau daya yazo gidan nan”

      Ni ba ruwana Inna yanzu ma gidan bikin kawata ya kaini daga can nake”

      Lumshe ido Khadija tayi sannan ta mike tabar dakin”

  Itama Samha Bata jima ba tabi bayanta, yayin da tana sa kafar ta adakin Khadija tace”

     Shi yace miki kizo nan??

    Jimmm tayi cikin ranta take cewa waye take nufi?? Wata zuciyatce tace koma waye dai ba’ace miki kizo ba, dan haka ahankali tace a’a daidai lokacin da take zama kusa da ita”

    Yasan Zaki zo???

    A’a ni biki yakaini fah Umma kuma sai 5 zai dawo kafin lokacin nakoma”

     To meye amfanin zuwan naki? Tunda yanzun shike dake Kuma beso kizo ba??

         Ni Umma bashi kedani ba, kuma inata cewa ya kawoni shine yaki”

     Bawani nan, munafuka kawai, tunda kina son shi sai kiyita zama, wato Dan ma karnace miki wani abu kika ko ki kirana awaya bare kizo, aini daman bace miki nayi dole ba, kuma ma tunda anriga anyi meye nawa kiyi zaman ki gidan mijin ki, kawai abun da narike ni baruwana dashi bazan hanashi zuwa nan ba tunda ba gurina zaizo ba amman Ina tabbatar miki inda Ina gidan mijina ne zance miki karya tako inda nake barema yamin rashin kunya”

    Kuka Samha tafara tana share hawayen take fadin”

    Nifa Umma wlh bakomai azuciyata bama guri daya muke ba yana gidan shi nikuma Ina wajen hajjah”

    Ainima bacewa nayi wani abu ba mara kunya zakice min wani yana gidan sa ke kina gidan Hajjah, ni Zaki rainawa wayau, shi din ne bansani ba ko kece bansani ba?, to ni karki jawo min abun mgn agari, azo aita zagina, auren ne nace karki yadda ayi bakin zama agidan miji ba, wato kinki zama agidansa sabo dani, ai gidan Hajjah ma gidan auren sa ne  tunda kina zaune agidan Hajjah kamar dakinsa kike,  ni karki gogamin kashin kaji, ni yanzun hankalina ya kwanta lfy Lau nake zaune, mijin ki kadai ke banson gani”

     Kuka kawai Samha keyi yayin da Khadija tace kitashi ki tafi ni babu ruwana”

     Hawayen ta goge sannan tace nidai Umma dan Allah kiyi hakuri wlh ba yadda kikace bane, ko Abbana ma sau daya ne naje nida Uncle”

      Hmmm wai Uncle, idan nasakejin kince min Uncle dinan saina daki bakin ki”

   Mikewa Samha tayi ta fita cikin Kuka sosai, damuwan data shiga bazata iya komawa gidan bikin ba dan haka kawai ta tari mashi ta wuce gidan Abbanta”

    Aunty kadai ta samu Bayan ta rungumeta tace daga Ina kike?, Kuma Ina mijin ki??

      Cikin kuka tace ni gurin Abbana naxo, ganinta cikin tashin hankali yasa tai saurin Kiran Abbanta domin kuka take kamar ranta xai fice”

       Cikin kankanin lokaci ya iso, tsaye yayi akanta yace yaya akayi Ummee??

     Mikewa tayi tafada jikinshi yayin daya rungumeta yana shafa bayanta, babu alaman wahala attare da ita, tayi haske tayi kiba gashi tayi shigar mutunci da Kamala duk wanda ya ganta sai yayi tunanin gin data fito, wannan yasashi ajiyan zuciya sannan ya dago yace mata Ina Ahmad din??

     Yana Office”

    Yasan kinzo nan???

    Kaita girgiza tare da fadin A’a”

    Toh meyasa zakiyi haka Mamana?? Inace namiki fada akan haka??

    Hawaye ta share ai gidan biki ya kaini kuma yanzun kafin ya dawo nakoma”

     Kash😬😬 wannan ba abu mekyau bane Mamana, kinason azageni ko??

    Kaita girgiza tare da fadin A’a”

   Kinaso mana, yanzun meye to meya kawo ki???

     Kukanta ta tsananta tare da fadin”

     Mamana ce”

    Mamanki??, Juyawa yayi ya kalli Aunty sannan yace bamu guri”

     Bayan wucewan aunty yace Ina Jin ki”

       Abba fushi take dani, nabata hakuri taki hakura, Wai Wai bantaba kiranta awaya ba bare inzo, kuma ni ba inda nake zuwa amman taki”

   Jimmm yayi sannan yace kinje wajenta ne??

    Eh

  Yaushe?

  Daga can nake??

    Au kin sata hanya kinje can sannan kikayo nan dan rashin hankali?, Wacce irin yariya ce ke ne??

   Mikewa yayi ya zura hannunsa aljihu sannan yace tashi muje”

     Ita da Abbanta tafe cikin mota yayin da yake fadin”

   Mmn ki ki rabu da ita zan ganta, nima tabar daukan wayata, ita har gobe tunaninta na yara ne, Amman zanje har gida ki kwantar da hankalin ki kinji ko, har kofar gidansu Zainab yakaita sannan ya juya ya tafi”

      Lokacin harsun gaji da nemanta kowa tambayanta yake daga Ina take dan lokacin 6:30 pm”

     Cikin kawar dakai tace gidan Abbana naje”

      Caf di Uncle dinki yafi awa acikin mota yanata Kiran number baki dagaba”

          Yawo ta hadeye domin ita tama manta da wata waya, cirowa tayi ta kirashi Saida ta kusa katsewa ya dauka cikin kausa saskiyar murya yace kina Ina???

        Gidan su Zainab”

         Ok kin dawo kenan??

    Daman ba inda naje…….

    Katsewa yayi, cikin kankanin lokaci ya iso, daman suna nan waje dan haka ta bude motar ta shiga, bece Mata kalaba be kuma kalli inda take ba”

     Gudu kawai yake Yi har ya fara bata tsoro kamar be damu amutuba, gajiya tayi da irin gudun tace”

      Uncle ka tafi ahankali”

      Ko ummhimmm bece Mata ba ganin sun wuce gidan Hajjah ta fara hawaye da alama gidansa zai kaita”

     Ganin isowan su gidan ya daga hankalinta, budewa yayi ya fice afusace yake tafiya

Itama sakkowa tayi ta gyara mayafinta, balakin tsoron shiga take idan ta tuna yadda ya Mata waccen karon, Hajajjh ce ta ceceni, nan ko babu kowa dagani saishi sai me gadi, kome zai faru idan na shiga?…….

3 comments

  1. Pingback: protein
  2. Pingback: Sciences_2025
  3. Pingback: dultogel

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *