Advertisements

BUGUN ZUCIYA PAGE 3

BUGUN ZUCIYA PAGE 3

Posted by

BUGUN ZUCIYA PAGE 3

 

Advertisements

BUGUN ZUCIYA

( Heartbeat)

Fadeela Lamido*

Advertisements

 

7 to 9

 

Advertisements

Murmushi yayi kadan batare da yace komai ba, binta da wani mayan kallo kawai yake”

Ma’u ko duk ta firgice tana rokon shi ya sakar mata hannu”

Mikewa yayi tsaye batare da ya saki hannun ba, kuma har yanzun idonshi na kanta wani maya tatcen kallo yake mata”

Cikin wata irin murya da bazata iya tattance yanayin sa ba yace”

Ke baby natsu, bason gaddama, kishiga hankalin ki, kinji ko?

Hannunta tasa duk 2 ta rufe bakinta tana daga kai alamar eh, acikin zuciyarta ko fadi take tawa ta kare”

Menene sunan ki?

Cikin rawar baki tace Asmau”

Lumshe ido yayi sannan yasa ke cewa menene ya fito dake yau bayan babu mkrnt?

Dan Allah dan darajan annabi kayi hakuri wlh daga gidan kakata nake, nasan yanzu tanacen tana nema na”

Cikin wata irin murya yace baruwa na da wata kakarki ni ke kadai nasan…..

Kukane ya kwace mata, cikin kukan tace to aini ban sanka ba wlh tsautsayi ne kawai ya kawoni nan, wlh da nasan haka ne da banzo ba”

Murmushi ya sakeyi ahankali ya kara runtse hannuta cikin nashi, tare da lumshi ido”

Zuwa can ya bude yace inace kinzo gadi nane?, dan kada abokan gaba su kawamin farmaki, dan kinsan nifa nauyin bacci gare ni, ke fah?

馃槴 Nima inada shi wlh, narantse inada shi”

Wannan karan saida yadan dara sannan ya dan jawota jikin shi tare da fadin baby ki kwantar da hankalin ki, bazan miki komai ba, jarumtar ki ta birgeni, ni jarumi ne dan haka inason naga mace jaruma, kin yi kokari sosai dakika tunkare ni, amman meya hana kika kasa hakuri zuwa gobe asabar kika fito yau?

Ainace maka gidan kakata naje yanzun ma tsautsayi ne ya fito dani”

Hmmm kawai yace sannan yaja hannuta zuwa gurin kwanciyar shi ya zaunar da ida”

**

Aban garen dada kuwa da misalin 12:09 sallama alhaji ne ya tasheta daga bacci”

Afirgece ta tashi tana fadin takwara shine baki tasheni baccin ba bayan kinsa ina tafiya masallacin juma,a da wuri”

Gaba dayan su wurga ido suke suga ta ina ma’u zata bullo daga abba har dada”

Jin shiru yasa dada ta shiga kwala mata kira taji shiru, mikewa tayi azabure tana fadin zoka zauna inaga ta shiga gidan tabawa bari nakirata”

Zama yayi kamar yadda dada tace sannan ya cire hular kansa ya aje agefe, tare da fadin Hmmm Allah ya kyauta”

Lokacin da dada ta shiga gidan ta bawa cemata tayi ko kallita bata gani ba, dan haka tayo waje hartana tuntube”

Azauren suka hadu da dan tabawa yana kokarin shiga gidan, kallon shi dada tayi tace kai iro baka gamin Asmau ba?

Aiko dazun naganta nan wajen hanyar mkrtnr su……

Bata bari ya rufe baki ba tabi hanya tana gudu2 sauri2″

Kalu innalillahi wa Inna ilaihir raju’un ta fada lokacin da ta hango ma’u rike hannun Duna”

Jikintane ya fara rawa bata San sanda ta kwasa aguje ta nufi gida ba”

Ganin dada agoje abin yabawa iro daya biyo bayan mamaki, shan gabanta yayi dan gudun karta tuntsura, riketa yayi tare da fadin dada lfy menene ya faru?

Ajiyan zuciya ta fara bata iya cewa komai ba saijan hannun iro take”

Daga nesa tamai nuni dasu, lokacin suna zaune ita da Duna”

Salati yayi sannan yace dada, ki tsaya inwuce saiki kwala mata kira tunda ke tsohowa ce kila bazai miki komai ba, amman ni idan ya ganni akwai matsala dada, tunda shi fadan shi baya wucewa inda kikasan shedan haka yake, cikin sauri iro yabar wajan yana me Kara karfafawa dada guiwa da hannun shi”

Tashin hankali ne sosai azuciyar Dada, kafafuwanta banda rawa babu abinda suke, kallo ma’u tayi tana mamakin yaya akayi ma’u tasan deeni harta bari suka zauna guri daya , kuma da alama ba tursasata yayi ba, kawar da tunanin tayi sannan ta daga murya ta kwalawa ma’u Kira”

Tana hango dada ta mike azabure, ta nufota aguje, ganin haka duna ya mike ya biyo bayanta”

Takaici ne ya kama dada dan haka ma’u na isowa ta daga hannu ta sharara mata mari, hannu ta sake dagawa zata kara mata, taji andaka mata tsawa cikin wata irin murya ta kyauraye”

Ke ! Ke!! Yasin yasin kika sake hannunki ya kara kaiwa jikinta sena sassara ki, Allah wlh *gunduwa gunduwa* zanyi dake, yasin hannunki ya kara kaiwa jikin ta kigani”

Suman tsaye dada tayi, fita tayi daga hayyacin ta, lokacin da network dinta ya dawo gani tayi suna tafe ita da ma,u sai janta take, tana kara fadin dada taho mana”

Bata iyace mata komai ba illah binta da take da kallo, sai dai akwai tashin hankali karara a idon ma,u”

Sauri ta kara dan sai yanzun ta tuna abban Asma’u yana gida yanajiran su, jitayi kaman lema ajikinta dan haka takai idonta kan zaninta jike yake sharkaf nan ta tabbatar fitsari ne”

Suna karya kwanan layin, ma’u ta hango abbanta sai zagaye yake akofar gidan dada, gefen shi iro ne azaune ya rafka uban tagumi”

Hunnun dada ta matse tare da fadin wayyo Allah na, nashiga uku”

Kallota kawai dada tayi ta tabe baki tare da fadin Hmmm”

Jikin ma’u ban da rawa ba abinda yake, cikin mtsanan cin tashin hankali ta taja ta tsaya tana me tsiyayar da hawaye dan ta tabbatar yau kashinta ya gama bushewa”

Ganin abba na tahowa yasa ta faraja da baya ahankali, tana kokarin rike Dada”

Yana isowa yasa hannun shi ya rabata da jikin dada ya zaf ga mata mari har saida ta fadi kasa, cikin karaji yace daga gidan uban wa kike?, jin da yayi babu amsa yasa ya daga kafa ya nufi cikinta yana kokarin tokarin ta aciki, tare da fadin badake nake mgn ba?

Cikin matsanan cin firgici dada ta rike Abba da wani irin karfi da batasan tana dashi ba, tana fadin kasheta zakayi ne?, toh bismillah nunamin yarka ce, nace kanuna min ka haifa kuma ni mahaifiyar ka ban isa na aiki yar ka ba”

Sanyi jikin Abba yayi, cikin natsuwa ya shiga bata hakuri, badan ya yarda cewa dadan ce ta aiketa ba”

Haka dada taita fada abba nabata, hakuri da karshe da kanta tasa ma,u amota abban ta, tana cigaba da fada”

Dada na tsaye akofar gida har motan abba ta bace, ajiyan zuciya ta sauke sannan ta juya ta shiga gida tana mamakin inda ma,u tasan deeni”

Kulle gidan tayi da sakata domin ita har yanzun gani take kamar duna zai shigo mata gida dan ba karamin tsorata tayi ba, wanka tayi ta gyara jikinta sannan ta wanke kayan da ta cire ta shanya, aranan dada bata runtsaba data rufe ido duna take gane”

Asmau kuwa suna isa gida ta sauka aguje tayi cikin gida”

Binta da kallo Abba yayi tsananta me tsanani yaji acikin ransa dan haka bayan ya shiga falon ya zauna, ma’u daga daki taji yana waya yana fadi”

*Usman* na gari ne?, toro mun shi yanzu yanzun nan, akwai matsala”

Faduwa ma’u tayi daga kan gadon dan ta tabbatar yau sai dai buzun ta indai ta bari har ya usman ya riketa”

*WAIWAYE*

Alhaji sani haifaffen jahar Kano ne, su 2 iyayen su suka haifa, daga shi sai yayan shi Alhaji musa, alhaji sani shine mahaifin Asmau, su uku suka haifa, tare da matar sa Fatima, usman shine babban, sannan fiddausi sai yar auta asmau wacce taci sunan kakanta”

Shiko alhaji musa Saida ya shikara 15 be samu haihuwa ba, dan haka kaninsa alhaji sani ya bashi danshi usman alokacin yana da shekara 5″

Usman ya taso cikin gata gidan alhaji musa tamkar dan da suka haifa da cikin su, yayin da alhaji sani yaci gaba da kula da fiddausi wadda take yar shekara 2″

Alharji sani da yayan sa ma,aikatan gwamnati ne, kuma suna samu daidai gwargwado dan a unguwar su idan xa ai lissafin masu hali baxa a kirga 5 babu su aciki ba”

Fiddausi nada shekara 10 aka haifin Asmau, tun daga kan asmau basu sake samun haihuwa ba”

Bayan shekara 8 fiddausi ta zama cikakkiyar budurwa meji da kanta duk abin da take so shi ake mata, saidai abu daya abban su baya barin yawo indai ba gidan dada tace zataba ba a barinta zuwa ko ina, dan haka lokacin da ta kare secondary ta samu daman tafiya jami’a ta balle bishashanta acan, ahankali fiddausi ta zama bata da abokai sai maza, haka zaka ganta tsakiyar maza ita kadai mace”

Babu wadda keda lbrn halin da fiddausi take ciki amakaranta, dan da antashi gida take yowa dan tasan ko minti 10 takara sai ance inata tsaya”

Ana haka maza suka fara canzawa fiddausi tunani domin ko duk abokanta kusan su 7 babu wadda baya lalubeta da sunan wasa, dan haka ta farajin babu abin da take so illah taga ta kadai ce da namiji”

Duk abinda suke sauran dalubai na kula dasu, yayin da wasu daga cikin matan suke tur da halin fiddausi, ita kenan yau ka ganta manne jikin wancen gobe jikin waccen”

Yauma kamar kullum tana cikin motar wani abokinta KB suna manne da juna ita da kanta ta lalubo bakin shi ta cusa nata ta, saida suka gama shagala, sanna ta gabatar mai da kudurinta”

Murmushi KB yayi dan yasan za’ai haka, yayi mamaki ma da har aka kawo yanzun bata bada kai ba, sabo da salon da suke mata”

Kwantar dakai KB yayi tare da fadin babu damuwa, amman fa saidai kizo muje Ki tayani kwana”

Zaro ido tayi dan tasan zancen shi bamai yuwuwa bane, tace KB ? Kana son Abbana ya kasheni ne?

Tsaki yaja sannan yace haba meyasa kike abu kamar wadda bata waye ba, ai dibara zaki masa”

Bayan kwana 2 fiddausi ta kasa hakuri dan haka ta shirya tayi sallama akan zata gidan dada ta kwana”

Gidansu KB ta wuce wadda har ya kaita da kwana adakin kb kuma har komai ya kasan ce, karfe 7:09am ta isa gidan dada da kayanta ajaka kamar yadda ta shiryu, ganin inda take tattale kafa yasa dada fadin ke lfy meya sameki kike wani tafiya saikace agwagwa”

Akafa fah na taho dada wlh gajiya nayi”

Ruwan wankan dada ta juye tayi wanka tare da gasa jikinta, ko karyawa bata tsaya yi ba, ta haye gado sai bacci domin KB be bari ta runtsa ba”

Damisalin karfe 8 alhaji sani ya iso gidan ganin fiddausi agado hankalin shi ya kwanta”

Tun daga ranan wannan dabi’a ta zaman mata jiki har saida ya kasance gaba dayan su 7 sun gama sanin wacece fiddausi”

Ankwashi tsayon watanni ana haka kullum fiddausi tana hanya wata rana takan kwana gidan dada amman sauda yawa dakin samarinta take wucewa idan ko har ta kwana gidan dada toh safiya nayi zata wuce gurin samarinta, babu wadda ya lura da halin da fiddausi take ciki har saida fiddausi ta fara rashin lfy, ana zuwa asibiti gwajin farko aka shaida musu tana dauke da ciki Wata 2″

Mummunan tashin hankali suka shiga ba kadan ba, wadda da takai har abba ya kwanta asibiti saka mukon hawan jini daya kamashi,

Duk abinda ake usman bashi da lbr dan lokacin yana mkrnt yana kokarin karasa karatun shi na soja”

Bayan abba ya samu sauki ne suka zauna da yayan shi alhaji musa tare da sanya fiddausi agaba ta fada musu wadda ya mata ciki”

Tashin hankali ba’a sa maka rana nan idon fiddausi ya raina fata damin kuwa acikin abokanta guda 7 babu wadda baya kusanta ta dan haka batasan sunan Wa zata kira ba

 

 

 

Heartbeat
Mmn Yazeed

57 comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *