Advertisements

IMG 20220121 WA0314

WATA FITSARA PAGE 21

Posted by

WATA FITSARA PAGE 21

 

Advertisements

WATA FITSARA

     By
Fadeela Lamido

                           Page 21

Advertisements

Cikin sauri ya dago ya kalli Hajjah, adaidai lokacin Daddy ke fadin”

    Wacce irinyar tambaya ce wannan?, Inace Fatima diyar Khadija ce??

     Cikin sanyin jiki tare da tuna abun daya faru tsakanin su dazon tace”

Advertisements

        Hakane Ahaji, abin dayasa kaji nayi zancen yariyar Ina sonsa da ita sosai kuma shima atunanina yana son yariyar dan yana nuna kulawan sa akanta tun tana karama”

    Murmushi Daddy yayi Banda abunki ai maso uwa yaso ‘ya’yanta wannan ba wani abu bane kawai kyautatawa ce”

   Jimmm Hajjah tayi sannan ta dago ta kalli Ahmad tace”

     Yanzun Kai Yaro Khadijar dai kake so tsakani da Allah Khadija tama girma fah🤔

    Hmmm Khadija guda nawa take, kawai saidai ace ta taba aure harda ‘yarta shikuma saurayine betaba aure ba amman duk da hakan anayi ai”

     Shiru Hajja tayi zuwa can tace”

     Toh Kai Ahmad Banda abun ka ai karamar yariya zatafi maka”

    Sai yanzun  Ahmad yadago kansa sosai ya kalli Hajjah yace”

        Hajjah itama fah Khadija  yariya ce har yanzun aini gani nake ma Fatima tafi Khadija hankali kinsan ita fa tun tana karama Bata da wani wayau kuma har yanzun ahaka take”

     Fashewa da dariya Hajjah tayi batare data shirya ba yayin da Daddy ya murmusa tare da cewa”

      Toh kindai ji ya gaya miki daman ai bawani girma tayi ba Ahmad idan Khadija ta tsufa kaima ka tsufa ai kawai dai aurene tayi takuma haihu Kai bakayi ba”

    Hmmm Alhaji kuma fah Ahmad da Khadija bashiri suke ba ko dazon Saida sukayi tsiya kaca kace da ita agidan nan”

      Hmmm wannan kidaina kawoshi aranki, ni banyi Mamakin Jin zancen aure tsakanin sa da Khadija ba domin yana nunawa tun besan kansaba nasan yana sonta tunanina lokacin kuruciya ke damun sa, kuma rashin Shirin nasu ai bayan aurenta ne”

    Hakane Hajjah tafada takarewa Ahmad kallo, sannan tace toh yanzun Kai yaya, ita Khadija ta amince maka?

     Kaitaye yace ta amince”

   Jimmmm Hajjah tayi sannan tace amman dazon fa naga kuma fada??🤔

    Daddy ne yace wannan ba matsalar ki bace Ahmad jeka zan nemi Alhaji muyi mgn”

   Godiya Ahmad yayi sannan ya mike ya fice”

      Tabe baki Hajjah tayi bayan fitansa ta kalli Alhaji tace”

     Ahmad yana da matsala wlh inashi Ina Khadija?

    Hmmm kibar ganin haka, shiyasa yakiyin aure hankalinsa yana kanta koda yaushe”

     Toh Alhaji itama Khadija ai antsayar mata da biki fah🤔

        Hmmm mubarwa Allah ikonsa kawai domin dazon Alhaji yake sanar dani tace ta fasa”

    Ta fasa? Auren??

   Kwarai kuwa, ransa abace sosai yana korafin tadade ahaka”

    Shiru sukayi gaba dayansu zuwa can Hajjah tayi ajiyan zuciya tare da fadin Allah ya zaba mana abun dayafi Alheri”

Kiran sallah dataji cikin kunnenta yasata saurin tashi zaune addu’a dauke abakinta”

     Bayyan ta tabbatar daga bacci ta tashi jammm tayi tunanin ta yaki zuwa gaba daya kanta ya kulle takasa yin ko wanni irin tunani”

    Kafarta ta sauke akan gadon tare da shafa fuskanta, gaba daya ji tayi fuskanta ya kunbura”

    Jimmm tayi tasan tabbass mafarki tayi Amman abun da ya daure mata Kai sosai”

         Fitowa tayi tsakar gida hango Babban tukunyan datayi kan murhu ya fara dawo Mata da komai daya bayan daya”

     Wogawa tayi ta hango tulin kayan wanke wanken yasa ta dafe kirjin ta, jiya fah an daura auren Ahmad da Samha😳

    Ahankali komai ya shiga dawo Mata, cikin daki takoma ta zauna tana me tariyo mafarkinta daya bayan daya, Inama mafarkina zai zama gaskiya, inama ace lokaci be kure min ba, hawaye taji yana zobo Mata tasa hannunta ta share tun lokacin data ji an daura Auren Ahmad da Samha ta rufe kofa cikin bakin bikin ciki da takaici tare da zubar da hawaye har yamma Bata bude kofa ba har bacci ya dauketa wadda ta shiga mafarkin duk abun da yake faruwa mafarkine, sai yanzun ta tabbatarwa Kanta ba mafarki take yi ba auren Samha da Ahmad anriga an daura kamar yadda ta sani jiya, tunanin da ta dingayi bayan Jin daurin auren yasata yin mafarkin komai daya faru a mafarkine”

     Tunu yadda Ahmad yayi Mata cikin mafarkimta yasata saurin runtse ido tare da cire tunin cikin ranta, hawaye ne masu dumi suka zubo mata tasa hannun ta share tare da hadiyar yawo domin makogoronta bushewa yayi sosai”

     Ji tayi gaba daya batason tuna komai domin indai tabiyewa zuciyarta komai na iya faruwa duk da tanaso abun ya kasance mafarkine gashi tayi mafarkin kuma tashi tasameshi a yadda yake saima dada lalacewa wasu abubuwa da ta gani wadda Ahmad din ke yi mata”

    Runtse ido tayi domin tuno yadda Ahmad din yai Mata cikin Baccinta lallai idan akacigaba Ahmad bakaramin wulakanci zaiyi mata ba shida Galadima”

    Zuwa wannan lokacin zuciyar Khadija ta kekeshe ta bushe duk dunkya ji take ta tsani Ahmad tsana me tsanani irin wadda ko Usman batajin ta tsana haka”

    Bata fito dakin ba Saida ta
Ta dake wa zuciyarta, afili tace”

    Wato dai Ahmad ya Aure Samha, Usman ya rufe idonsa ya ture komai ya Aure masa ita duk da cewa tana ‘yar kankanuwa be damu ba sabo da ya baganta raina”

     Amman bakomai, mgnr zuciya ne take yinsa afili, bakomai Usman tunda nika wulakanta ba Samha ba, nasan Allah ne ya baka dama, zaka iya yin duk abun da kaso lokacin ka ne, tsaki taja sannan ta fita har yanzun garin be gama wayewa ba”

    Alwala tayi sannan ta nufi dakin Inna tayi sallah sannan ta gaidata”

     Cikin sanyin jiki Inna tace”

    Khadija ki dinga sausautawa kanki, ki rage saka damuwa cikin zuciyarki, Jiya tun bayan daura auren nan kika rufe kofa kowa sai tambayan ki yake, tsakani da Allah Ahmad be cancanci haka ba awajen ki, kince baki son auren ne saboda ya nuna yana son ki kuma yanzun yadawo yace Fatima, wannan bawani bakon abu bane anayi , musulunci ya yadda da hakan Banga dalilin tada hankalin ki ba”

     Cikin kawar dakai tare da dakewa Khadija tace”

    Shikenan Inna nagane”

   Yauwa ko kefa, jiya da zamuje dauko amaryar akace Uban yace da kansa zai kaita daga baya kuma Alhaji yace yabugo masa waya Bata da lafiya sai yau za’a kaita”

    Jimmm Khadija tayi tana tuna yadda taga Usman yakaiwa Ahamad Samha cikin mafarkimta kawar dakai tayi sannan tace”

         Allah ya saukake”

   Mikewa tayi ta bar dakin yayin da tana shiga daki ta Kira Samha”

  Kamar jira take ta dauka cikin muryan dataci kuka ta koshi tace”

      Umma?

     Samha, akace baki da lafiya?

     Fashewa tayi da kuka”

    Jimmm Khadija tayi tana sauraronta sannan tace”

     Kiyi hakuri Samha ki daina kuka, duk ninaja miki wannan abun, meke damun ki yanzun?

     Kainane yake zuciwo Umma sannan kuma komai bayai min dadi, banajin Dadi sosai”

    Kinaji Samha, kiyi hakuri kawai, nasan duk rashin son auren da kike baki kaini ba, Babanki yana da naci duk wani abu da zanyi in nuna kina ga auren nan nayi Amman Saida aka daura bare Kuma ke Samha, tunda har Abbanki yaki sauraron ki aka daura auren yanzun ma bazai saurareki ba, shikenan kije kinasa abun da ransa yake”

    Kara karfin kukanta tayi yayin Khadija taci gaba da rarrashin ta”

    Bayan ta aje wayar nutsuwa tayi sosai tana tuna yana yin girman Samha tare da girman Ahmad afili tace yanzun shi Ahmad Dan bashi da kunya saiya neme Samha?, Maji magani, gashi ga Samhar nan, Dan iska kawai mara girma wadda besan ciwon kansa ba”

         Ahmad kwance gidan Hajjah yayin dayai balakin kosawa Yasa Fatima cikin idonsa barin da ayanzun be wuce yaga gashi ga Fatima ba, sosai yasa rai da ganinta ajiya amman saiya samu lbrn Bata da lafiya hakan ya Kara daga hankalin sa sosai da sosai”

     Ayanzun haka yana kwance ne zazzabi na nemam rufeshi sosai yai balakin kosawa ya ganshi kusa da Samha”

   Misalin 4 na yamma Alhaji Usman ya isa gidan Momy lokacin mutane sun fara watsewa saina gida gida kawai”

     Zama yayi kusa da Momy sannan yace”

    Inna Ummee??

    Tana ciki ta fada cikin yanayin damuwa”

    Toh ya jikin nata?

    Ta samu sauki bakamar jiya ba”

     Kawar dakai yayi sannan yace toh ashirya min ita mu wuce”

   Jimmm Momy tayi ko za’a bari zuwa gobe lokacin ta
Kara warwarewa”

   Momy idan taje can ta warware baki daya, duk inda hankalin mijinta yake yanzun nasan yana kanta dan haka gara mu bashi matar sa”

   Jimmm Momy tayi sannan tace”

    Amman ga wani hanzari ba gudu ba, tunda aka fara zancen nan banji ka Kira sunan Khadija ba kuma itama tana da hakki akan ta domin ita ta haifeta Ina fatan kayi shawara da ita”

    Cikin kawar dakai yace, Momy Khadija batason wannan auren itace ma take hurewa Ummina kunne”

     Toh meyasa akayi Usman ?

   Yanzun Momy Dan Khadija bataso sai afasa, itafa yariyar tana sonshi Momy bansan yadda akayi ba Khadija ta samu kunne ta ta hure, kuma ita zata jawa wahala donim dai aure an riga da andaura mijinta kuma dole ta masa biyayya ko musamu matsala ni da ita”

    Jimmm Mommy tayi sannan tace”

    Amman duk da haka kabata hakkinta, yanzun kafin ka kaita kabiya tasa masu albarka inda hali ma kuje ku kaita tare tunda yanzun anriga anzama daya aure an riga andaura ita kanta bazata so ‘yarta ta zama bazawara ba to ataru ayi hakuri sai muyi addu’a Allah yasa hakan shine mafi alheri ga rayuwar su baki daya”

    Cikin yanayi irin na me tunani yace,”

    Toh naji momy zan biya, Amman nasan Khadija bazata bini mu raka Ummee ba, sannan baxata fadi alheri ba domin nafi kowa sanin taurin Kai irin na Khadija, wadda take son ta koya Ummee”

     Tabe baki Momy tayi ko ku koya Mata ba, ai Kaima haka kake saidai Allah ya kyauta”

Alhaji Usman shi da Samha akan hanya, Babban hijjabi ne ajikin ta wadda Ahmad ya zubo cikin lefenta babu gyale ko daya cikin kayan”

      Sosai hajjibin ya karbi jikinta yayin da Abbanta ke kallonta ta gafen idonsa yana murmushi domin wani kyau dayaga ta Kara tare da girma”

      Akofar gidan su Khadija ya tsaya sannan yacewa Samha ki shi ciki kice Mata gani inason ganinta”

       Ahankali tace tam tare da sauka harta shi gidan yana binta da Kallo”

     Adakin Inna ta sameta yayin da kowa ya fara murna ana amarya amarya”

     Ganin Wai Khadija ake cewa Amarya wani abu ya tsaya Mata awuya bayan sun gaisa ta da kowa ta kalli Khadija tace Abba na kiranki yana waje……

     Bazani ba lallai ma bashi da hankali”

     Binta da kallo akayi yayin da wasu daga ciki suka shiga yi Mata fadan ai an riga anzama daya ya zakice bazaki ba”

    Cikin fushi ta miki ta dauki Karamin hijjabi tasaka ta fice”

   Khadija na dososhi ya fara murmushi, tare da kafeta da ido harta tsargu da kallon”

     Tsaye tayi yayin tayai wani irin kafeta da ido zuwa can ya harde hannunsa akirjinsa yanai Mata kallon kasan ido yayin da Khadija ke kauda kanta can gefe”

      Zuwa can taji yace Allah ya huci zuciyar ki Khadija, idan kina fushi kinfi kyau, amman wannan karon naga kamar har tiriri kike, duk da hakan ma dai kinyi kyau babu laifi”

   Kallonsa tayi da niyar masifa Amman ganin inda ya tsareta da ido tai saurin cire idonta tare da fadin”

    Duk abun dakace daidai ne, yanzun meya kawo ka gidan kallo kazo ko kazo ne ka Kara tura min wani bakin ciki?

    Murmushi shi ya fadada a’a nina zone mu raka kayan mu gidan mijinta”

     Kai dawa??

     Nida wadda muka Samar da ita..

      Toh bazani ba”

    Kiyi hakuri muje mana”

     Bazani ba nace mika, lokacin da ka Mata auren aiba Dani kayi shawara ba, babu ruwana kaje ka riketa nabar maka, karka sake zuwa wajena dama Samhace atsakanin kuma yanzun nace nabar maka, karkara tuna ni bare har ka nuna ka sanni, niba uwarta bace ba Kaine uwarta Kaine ubanta nabar maka Tunda ka nuna bakasan darajata ba”

   Cikin murmushi yace nafi kowa Sanin darajar ki Khadija sanin Darajarki yasa na yanke wannan hukuncin kuma tunda kince min kin barmin aini nagode, karki manta Nina mijine ba mace ba, bare abun ya dameni, ince kar Ummee nan gaba tace min Bata da Uba, yanzun ko ko ita tasan ke kika haifeta kuma duk wadda yasan Fatima yasan kece uwarta yanzun tana cikin shekara na 17 kinga ai saidai nai miki godiga, cewa da kikayi kuma karna Kara nuna nasanki naji na yadda Amman a baki ko?, Domin kinsan a ido baya goguwa, nine mutun nafarko Dana fara sanin ki, ninasan dadin ki nakoyar dake komai, kika koya min komai kema, dake nasaba Khadija dan haka nafi kowa sanin ki, ko ayanzun da kike sanye da hijjabi atube nake ganin ki kinga kuwa karshen sani kenan”

      Cikin tsabar Jin haushi Khadija tace toh Allah ya isa dan iska kawai”

       Murmushi shi ya fadada tare da fadin”

    Kinci bashi”

    Juyawa tayi ta nufi gida afusace yayin dayabi bayanta da kallo harta kule”

      Tana shiga tacewa Samha tashi kije kibar wayarki abude zan Kira ki”

    Hawaye kawai Samha ta share sannan ta mike yayin da Inna da Inna Yalwa suka bita suna rarraahinta tare da zolayanta”

     Har gavan Motar Usman suka rakata tare dasa mata albarka daga karshe suka shiga zulayanta irin na kakanni”

   Murmushi Alhaji Usman yaitayi yayin da Samha take share hawaye”

       Bayan sun hau titi sosai Usman ya kalli Samha yace”

     Mamana?, Share hawayen ki, idan mijin ki yaga kina kuka ransa bazai masa Dadi ba”

      Hawayen ta shiga sharewa, Amman wasu yayin da wasu ke sakkowa”

     Yana kula da ita ransa baya masa Dadi saidai beson tagane hakan”

      Wani gida suka shiga shi kanshi Alhaji Usman gidan ya burgeshi yana tsayawa Ahmad na fitowa”

        Sakkowa yayi sannan ya rike hannun Samha ya nufi inda Ahmad yake”

    Juyawa sukayi gaba daya yayin da Ahmad ke mika gaisuwa cikin sunkuyar dakai”

       Ahankali suka isa katafaren falon da aka kawata da kaya irin na zamani, zama Abba yayi yayin da Samha ta zauna kusa dashi idonta akasa”

      Ahmad ma zamayi yayin da suka Kara gaisawa, nasiha Abba yayi masu sannan ya mike ya kama hannun Samha ya isa gaban Ahmad ya damka masa”

    Kan Ahmad akasa ya rike hannun Samha tare da yiwa Abba godiya”

     Abba najin ihun Samha cikin kunnuwan sa ya juya ya fita cikin sauri harya hau Hanya yanajin amon ihunta cikin kunnen sa”

      Hawaye ya zashare tare da yiwa ‘yarsa addu’a dacewa gidan miji, hawaye ya sake sharewa yayin da hakan yayi daidai da Karan shigowan sako cikin wayar sa”

    Wayar ya dauko ya duba sakone daga Khadija cikin sauri ya bude”

      _irin wannan kallon da kake min nima na sanka cikin irin wannan yanayin da kake fada, dan haka ka kiyaye irin kalaman da zaka dinga fada min_

   Murmushi yayi tare da fadin afili Khadija kenan, zagin da kika min besaki kin huce ba kenan”

       *********

   Ahmad kuwa runtse idon yayi bayan ya tabbatar Samha ce ahannnun sa, ikon sa ce mallakin sa ce, sai yadda yayi da ita ayanzun”

   Bude ido yayi ya sauke akanta sai share hawaye take, hannunta yaji zafi rau dan haka yai saurin Kai dayan hannun sa Kan wuyanta yace

     Jikin har yanzun??

   Cikin sauri ta ture hannun sa daga cikinta yayin da ya tsaya yana kallonta”

      Zuwa can yace Sannu Fatima, zazzabin ne kadai ko akwai inda ke miki ciwo???

      Banza tayi dashi tare da kokarin tashi”

    Ina zaki, Fatima bazaki min mgn ba?

      Cikin kuka sosai tace”

    Nibani da lafiya kuma bazan iya zama tare dakai ba”

   Jimmm yayi sannan yace toh dawa Zaki zauna Fatima???, Nifa mijin ki ne ayanzun?

    Kaita girgiza hawaye na zubo Mata”

       Kallo yabita dashi sannan yace”

    Niba mijin ki bane???

      Eh tace kanta tsaye”

     Jimmm yayi tare da tsurawa waje daya ido sannan ya kalleta yace shikenan naji niba mijin ki bane saiki gaya min ‘,yar wacce kikeyi dani, duk yadda kikace bani da zabi haka zanbi”

      Kawar dakai tayi, ni Kai Uncle dina ne”

    Toh naji Babanki kenan ko??

   Kaita daga masa yayin daya tsare ta da ido, acikin ransa yake fadin wannan tsarin Khadija ne dole na sake shiri, kallonta yayi yace”

   Shikenan na amince ke yariya tace4 bakiyin mijin dani dai ko?, Naji na amince ni Babanki ko?

      Kai ta sake dagawa sannan yace abu me sauki wannan ba matsala bace yanzun barin nemo miki magani kisha daga baya sai musan abun yi”

    Ni bazan sha magani ba”

    Kawar dakai yayi toh me kike so??

      Ni gidan nan ne bana son zama cikin sa”

   Jimmmm yayi zuwa can yace to tashi muje nakaiki Gurin Hajjah, amman saikin min alkawarin zakisha magani kuma zaki tsaya nai miki allura”

    Batare datayi wani tunani ba ta daga kanta, dakinsa ya nufa tare da fadin Ina zuwa”

      Zuwa can ya fito da makullin mota ahannun sa ganin tana rawar sanyi ya juya ya dauko katuwar rigar sanyin sa yace cire hijjabin kisa wannan sabo da sanyi”

   Mikewa tayi ta cire Hijjabin kamar yadda yace tasaka rigar yayin da rigar gaba daya Kamshin sa take bayan ta gama daidaitata ta dauki hijjabin ta sanya, Hanya ya Bata ta shiga gaba sannan yabita abaya yana murmushi”

   Acikin motar  ya shiga janta da mgn  saidai taki cewa kala har suka isa gidan Hajjah”

     Cikin fara’a sosai ta tarbe su yayin da take rike hannun Fatima tana fadin yaya dai Fatima?

    Hajjah har yanzun jikinta da zazzabi”

    Kallonta Hajjah tayi idonta jawur yayin da ta hango wasu Sabbin hawayen na zubo Mata”

    A’a Fatima yada kuka har yanzun kuma??

     Cikin kawar dakai Ahmad yace”

     Nine batayin mijin dani Wai, gatanan ma gurinki zata zauna”

      Dariya Hajjah tayi sannan ta kalli Samha tace”

     Fatima bakiyin mijin dashi wai??

     Kaita daga batare datayi wani tunani ba”

     Dariya Ahmad da Hajjah sukayi yayin da Hajja tace to me kike yi dashi??

        Kanta akasa tace Uncle dina ne”

      Kawar dakai Ahmad yayi yana murmushi yayin da Hajja tace”

    Kwarai kuwa Fatima, Baban kine Ahmad, ki kwatar da hankalin ki kinji, karki Kara tada hankalin ki,  kibar zubar da hawaye nan zamuyi zaman mu tare, juyawa tayi ta kalli Ahmad tace tashi ka nemo Mata magani jikin nata Kara zafi take……

3 comments

  1. Pingback: sagame
  2. Pingback: Plinko 1000

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *