Advertisements

IMG 20220121 WA0314

WATA FITSARA PAGE 34

Posted by

WATA FITSARA PAGE 34

 

Advertisements

WATA FITSARA

     By
Fadeela Lamiɗo

PAGE  34

Advertisements

Tun kafin Samha ta sauka cikin motar take kwarara amai Dan haka Saida driver yajira tahuta sannan ta fita cikin motar”

    Ruwa ya nema ya wanke wajen sannan ya koma gida”

      Koda Samha ta shiga gidan kanta tsaye ta wuce dakin Khadija saidai babu kowa adakin”

Advertisements

         Sanadiyar aman da taitayi miyau ne cike abakin ta kwanciya tayi tsakiyar dakin tana hawaye”

        Sosai gaban Khadija ya fadi ganin Samha yashe atsakar dakin ga amai nan agefenta Kuma sai gunshikar kuka take”

      Cikin kaduwa sosai tace kedawa Samha???

     Bakinta cike da yawo tace ni daya”

      Cikin sauri ta fita dakin zuwa can saigata tare da Inna da Kuma Inna yalwa”

       Dagata sukayi suna fadin”

    Babu lafiya Fatima meye haka”

     Gyara gurin suka shiga yi sannan suka hada mata ruwan wanka”

     Bayan ta fito rigar Khadija ta saka duguwa wadda tadanyi mata yawa gadon Khadija ta kwanta daidai lokacin da Inna tace”

       Ke Fadi Ina Ahmad din??

    Sabon kuka ta barke dashi tare da kudun dune kanta”

     Inna yalwa ce ta kalli Samha tace”

     Ku rabu da yariyar nan ta huta bafa kalau take ba, akwai alaman shigan ciki a tattare da ita……..

    Nashiga Uku Khadija ta fada yayin da su Inna suka maida hankalin su kanta bangane kin shiga uku ba???

     Kawar dakai tayi cikin tsananin fargaba tare da Mamaki tace”

     Inna abun ne yaban Mamaki Samha ce da ciki??

     Iyeee mana son kike taita zama haka aima tajima”

      Acikin ranta tace Cafdi afili kuwa cewa tayi Allah ya kawomu🤔🤔🤔 “

      Dariya Inna yalwa tayi sannan ta juya tana fadin ko tantama vanai yariyar nan ciki ne da ita”

      Juyawa itama Inna juyawa tayi tana fadin barin nemar Mata abun da zataci”

.     Tsaye Khadija tayi abakin gadon tana karewa Samha kallo afili take fadin”

      Ikon Allah sai kallo🤔🤔 kallon Samha tayi sosai sannan ta tuna Ahmad tace acikin ranta”

     Yanzun banda ikon Allah wa ya isa yai haka?, Wai Samha ce keda cikin Ahmad🤔🤔

      Sosai jikinta yai sanyi cikin yar siririyar muryarta tace”

      Samha tashi ki koma dakin Inna ki kwanta”

      Cikin muryan kuka tace ninafi son nan…….

    Bata ida rufe bakiba sukaji an shigo dakin afusace gani kawai tayi an finciko Samha dake kangadon kamar wata kaza, batare data tsaya duba ko waye ba tasa hannunta ta rikekita Karan mari taji ya sauka Dan haka ta daga kantan da sukayi Ido biyu Ahmad yana rike tam da Hannun Samha daya yayin da dayan yake rike a hannun Khadija”

        Saketa Khadija ta fada tana kallon cikin idon Ahmad”

     Cikin Jan Ido yace kinsan Abun da tamin ne??

       Koma meta maka  kayi hakuri Bata da lafiya”

        Zame hannunsa yayi sannan ya juya ya fita, karo sukaci da Galadima cikin harara yace Amman Ahmad bakajin magana hannun kawai Ahmad ya daga mishi sannan ya fita daga gidan”

      Bayan shi yabi ko kafin ya fita yabar layin gaba daya”

      Kwana Uku Samha tayi agidan Ahmad be sake lekowa ba kuma ko waya beyi ba wannan abun ya daga hankalin kowa agidan musamman Khadija domin tasan fushi yake da Samha”

      Tunda tazo gidan ciwonta Kara gaba gaba yakeyi kullum tsufar yau daban na gove daban”

        Kuka taji Samha nayi cikin tsawa tace Menene??

      Ni kafafuwa na ciwo suke min, Umma dan Allah ki matsa min”

     Zama tayi bakin gadon ta kama kafarta tana matsawa take fadin??

     Mijinki yayi fushi dake be dawo ba har yau??, Ya kamata ki kiraahi awaya”

    Nan danan hankalin Samha ya tashi nan ta fara hawaye”

  Kallonta Khadija tayi tace Wai meya hadaku”

    Ni Babu ruwana dashi Umma danma yasamu na zuna saiyaita min wani masifa Wai harda wani Wai aure zai Kara, wlh Nima bazan zauna ba”

    Tsaki Khadija taja sannan tace baki da hankali Samha, baki gyara hankin ki ba ko??

    Umma shine yake tsokanata fa”

   Karya kike Samha, nasan halinsa fiye da tunanin ki, kema Kuma nasan halin ki, nasan bazai tsokaneki fadaba saidai tsarinsa ya miki tsauri Kuma duk tsaurin da zai miki dole dole kibishi,  yanzun ki kiraahi cikin waya kibashi hakuri, ni Babu ruwana gashi naga alama so kike kidinga goga min kashin kaji, da kin tattaro rigimar ki saikiyo min nan kuma ki makale nan azu adameni da fitsara, ki kirashi nace”

    Kira taitayi harta gaji ba’a dagaba, wayarta ta mika Mata kirashi da tawa”

     Dauka yiyi cikin buguna Uku”

    Ahankali tace”

  Ina kwana”

   Kamar bazai amsa ba sai kuma yace lafiya lau, ya Mamanki??

    Lafiya lau”

      Jimmm yayi sannan yace toh yaya akayi???

    Inata kiranka da wayata baka daga ba?

    Mezakice min, keda kika gudu kika barni, kina neman ki maidani mahaukaci atiti, ai gaki ga Mamanki kiyi zaman ki duk ranar da kika shirya ki kirani na dauke ki, katse Kiran yayi yayin da Samha taji ba dadi”

      Ajiye wayar tayi zuwa can taga fitan Khadija ta sake dauka ta kirashi yana dagawa tace”

   Uncle kayi hakuri kaji”

    Naji sai anjima katse Kiran ya sakeyi, ganin haka hankalinta ya tashi sosai, tsintan kanta tayi da Kiran Hajjah cikin kuka take Gaya Mata tana gidan baba Kwana uku kenan bata da Lafiya”

     Cikin kaduwa sosai tace Kuma ko dazon Ahmad ya shigo gidan nan be Gaya min ba duk da dai cikin damuwa na ganshi”

     Misalin Karfe 2 Hajjah da Aunty Saude sukazo adakin Khadija suka Samu Samha tana ganin ta tace”

     Masha Allah Ina ‘yata, Yaro yana Inna begaya min wannan abun farin cikin ba🤔, Ashe dai zanga wannan ranar?

         Langabewa Samha tayi jikin Hajjah tana fadin”

     Ai fushi yakeyi Dani Hajjah ko zuwa ma beyi ba”

      Barni dashi Samha aiba a fushi da mara lafiya, wuni sukayi har yamma sannan suka wuce gida”

      Adaren ranar Ahmad yazo yanayin shi kamar mara lafiya, Khadija ya gaidar sannan ya juya yscewa Samha ya jiki??

       Amsawa tayi, ledojin daya shigo dasu ya kara matsowa dashi sannan ya mike yana fadin Saida Safe”

      Tsaya ka tafi da ita

     Cewar  Khadija”

    Dan juyowa yayi kadan sannan yace”

   Kibarta aitafi son zama wajen ki”

    Bangane tafison zama guna ba, ni karku sani acikin zancen ku, idan ba kana nufina da wata masifa ba ka dauki matarka ku tafi”

      Kibarta anan nina gaji”

   Runtse Ido tayi cike da baccin rai sannan tace”

     Ahmad ka dauketa ku wuce karka barmin ita anan idan har kanason ka nuna fushin ka akan wani abu da tamaka aisaika kaita gidan Ubanta”

   Jimmm yayi sannan ya dawo ya zauna itama Samha hankalinta tashi yayi ganin Uncle Ahmad da Ummatan kowa cikin Fushi”

    Bayan ya zauna yace”

  Ni ai nan din ma bani nakawota ba, ita ta kawo kanta nagaji dabin yariyar nan tan tana wulakantani, tagara ni nan da garani can, akanmu aka fara aure dazata dinga wulakantani, tsintan kaina kawai nayi acikin wannan rayuwar bani nasaka kaina ba kuma da mutun nada ikon goge abun da yake so cikin zuciyarsa da tunani na goge Fatima, niba Yaro bane nasan abun da nake cikin tsananin baccin rai yake mgrn yayin da jikin Khadija yai sanyi sosai”

     Cigaba yayi da fadin”

    Yanzun ba auren bane agbanta som zama tare dake take ta zauna din duk ranar da tagaji saita laluboni”

      Mikewa yayi har ya fita adakin tace”

    Yanzun wannan magan ganun da kakeyi dawa kakeyi. Su ni ko Samha??

      Ni da ita nakeyi badake ba”

    Toh kaxo ka tafi da matar ka ni babu ruwana”

     Zan dawo da daddare ya fada sannan ya juya ya fito”

     Yana fita Khadija ta kalli Samha tace”

      Kinason kiga baccin raina Samha”

   Wlh Umma ba abun da nake masa”

    Rufemin baki nasan yanzun haka akan irin wancen matsalar ne dayazo da ita kwanaki bazaki bari ba ko??, Toh Bari kiji daga yau bani bake sai ranar da kika daidaita da mijin ki, sannan daga yau karki sake fita daga cikin gidan ki batare da izinin mijinki.ba koda kuwa gidan Hajjah ne, nalura dake kina da taurin Kai cizo din ma idan kika Kara cizon mijin ki Allah ya isa ban yafe miki ba”

   Nibana cizon shi fah”

   Dallah rufe min baki, yanzun zargin shi ninake zugaki, shiyasa yabarki anan tun bayan auren nan nataba ce miki karki zauna dashi???

   Kai Samha ta girgiza”

    Toh meyasa kike nuna baza zakiyi va”

     Cikin kuka tace Umma ai to badan Allah yake Sona ba😭😭

    Inji wayene ya Gaya miki???

    Cikin kwalkwal da ido tace”

          Aidan kawai yabaki haushi ne”

   Innalillahi wa’inna ilaihir raju’un ta fada sannan tace”

   Samha baki Fahimcine baNe lokacin bani kaunar auren ne ko kadan, Amman tunbayan auren kinji nace miki karki zauna??, Naki auren ne lokacin sabo da wani ra’ayi nawa yanzun dai nace kibar mgnr”

      Umma cewa fa kikayi yanai miki rashin kunya kuma kikace ba ruwanki da auren”

    Idan da nace ba ruwana da auren yanzun akwai ruwana da shi, nalura kafiya gareki kuma duk fadan danai miki wancen karon bakiji ba, da alama har yanzun kina cizon shi??

     Ni banawani cizon shi fah”

    Dallah rufemin baki tunda ke kunnenki na Kashi ne, daga yau idan kika Kara cizon shi Allah ya isa Samha, kinajin maganganun da yake fada dazon ganin yake nike zuga ki, kidaina tuna komai ku zauna lafiya ni Babu ruwana nasan indai Dan tashine bazayi fadaba, nasan Dan ra’ayine wannan bazai zama matsalaba a karkashin sa kike dole kibishi, nagaya miki babu ruwana”

     Hawaye Samha take sharewa sannan ta juya ta kwanta tana me share hawaye”

    Itama Khadija mikewa tayi yayin da taji Munyar Samha tace”

       Umma??

    Na’am mene Kuma”

   Ranan nan da mukaje gidan Abbana Aunty batanan shikadai ne agidan”

     Lumshe ido Khadija tayi zuwa can tace Allah sarki”

     Shiru sukayi zuwa can Samha ta sake cewa”

     Umma?

   Na’am

   Sai yabani tausayi nasan kuma rabuwa suka yi”

      Gutun karta sake fadin wata mgnr tasake cewa Allah sarki”

     Umma dama dai ki koma gidan kawai……

     Samha banson surutu kitashi kifara shiryawa”

    Ai zan shirya Umma, kinga kema ke daya Abbana ma shikadai ne idan kika koma zaifi ai”

    Samha wlh zan mareki, tunda akanki nake ki daukeni ki kaini, Mara kunya kawai”

     Shiru Samha tayi cikin baccin rai zuwa can ta fara kuka sosai take son sukoma da auren su musamman yanzun  dataga babu kowa agidan”

      Tundaga lokacin Bata sakeyiwa Khadija mgn ba data shigo take dauke kanta, abun dariya ya soma bawa Khadija”

      Misalin hudu na yamma jikin Samha yai Mata sauki dan haka ta fito tsarkigidan inda duk aka taru ana hira, ciki harda Khadija yayin da wasu labarn da dama Khadija ce ke badawa yayin da aketa kwasan dariya kinyin dariyar Samha tayi duk da cewa hiran na Bata dariya, wani Yaro ne yayi Sallama Wai ana Sallama da Hadiza”

     Cikin sauri Samha tace”

   Babu Hadiza anan gidan”

   Gaba daya juyowa akayi ana kallon Samha data daure fuska, inna ce tace”

   Yaya zakice babu Ita agidan  uwar taki kika manta sunanta??

    Yaron ne yasake dawowa yasake cewa wai Khadija yace”

     Kai!! Dallah kace tayi aure batanan Samha ta sake fadi tame turo baki”

      Dariya mutanen dake wajen suka fara yayin da takawar da kanta can gefe taki dariyar, Khadija kuwa kasa motsawa tayi, Inna ce yace kemu kinaji anacewa kinyin aure”

     Mikewa tayi tace innajinta Inna, ai uwata ce  inaga, hararan Samha tayi sannan ta shige dakinta ta kwanta”
Itako Samha kin komawa dakin Khadija tayi, Sai can dare Ahmad ya shigo dakin Khadija ya nufa dan zaton sa tana can, sallama yayi bakin kofar ahankali Khadija tace tana gurin Inna”

        Toh yace sannan yadan tsaya yai jimmm zan iya shigowa??

    Eh tace ahankali shigowa yayi ya zauna, sannan ya gaidata”

     Lafiya kawai tace, kamar kamar yadda ta saba sannan yace”

    Nadawo in tafi da ita, Amman dan Allah Kimata fada kafin mutafi, wlh inacikin matsala sosai da ita”

     Kuje namata fada”

    Kansa akasa yace kiyi hakuri dan Allah da kibata”

Kawar da kanta tayi can gefe yayin da yakira Samha awaya cikin kankanin lokaci ta iso hijjabinta ta dauka cikin sanyin jiki ta sanya”

       Tabbatar wa da Khadija tayi jira yake yaji tace wani abu yasata fadin”

      Kindai ji abun da nafada miki ko??

     Cikin yamutsa fuska ta daga ganta”

    Kawar da Kai Khadija tayi sanan tace shikenan Saida safe”

     Har ransa yaji farin ciki mikewa yayin da ya kalli Samha yace Muje Hanya ya nuna Mata ganin tana tafiya ahankali ya roko hannunta yana fadin”

  Mun gode”

   *************

Tun amotar ya lura da canjin yanayin Samha, ta sake sosai dashi saidai kamar yadda Hajjah ta fada masa Fatima nada ciki shima sai yanzun ya lura”

    Bayan sun shiga gida wanka sukayi atare bayan sun fito kuwa sabon hirane ya barke atsakanin su kamar dai sun jima basu hado ba”

     Fatima ashe kallona ya shiga raga”

      Daman kana bugawa ne uncle??

     Eh mana Ina bugawa Amman ba sosai ba, kasa yayi da muryan sa yace kinji fadan da Mamaki ta miki zaki barni inbuga Babu takura??

    Me zai hana Uncle kayi abun ka tunda ba akaina zaka buga ba aida sauki”

   Marairaicewa yayi ajikinta yana fadin”

    Idan akanki zan buga ba??

    Toh ai Uncle kaina ciwo zai min”😫

     Ai bazayi. Saitin kanki ba”

      Toh adaidai Ina zaka kwalo min”

   Cikin murmushi sosai ya nuna kirjinta “

    Haba Uncle wannan ai muguntane ciwo agurin bakaramin zafi yake ba”

     Cikin Kara narke mata yace dan Allah?, Inace tausa ne kawai basai in tausa miki ba”

     Nonon nawa??

Toh meye ba kayana bane??

     Cikin sauri ta waiwaiga sannan tai saurin tura kanta cikin kirjin sa”

  Murmushi yayi sannan ya Kan kamsta akirjin sa yana fadin”

   Toh kunyan wa kikeji?, Mu biyu ne agidan, gidan mu ne dagani saike ki saki jikin ki kiyi abun da ranki ke so, nan din gidan mijinki ne Ina fatan miyi.kyakyawan rayuwa muda yaran mu, idan yaran suka mana yawa gidan ya fara kadan saina saya mana Babban gida”

      😳😳 Uncle yara Kuma har su cike gidan nan duk acikin wa?, Kasan ma kuwa su Inna nata cewa wai ciki nake dashi”

     Dan Allah zanyi farin ciki da hakan, yanzun inajinki bani lbr me Mamanki tace miki akwai na”

    Fada kawai tamin Uncle”

   Naji Dadi sosai da Mamanki ta fara sakkkowa Amman da harna bara tunanin tun farko ta tsaneni yake kawai take min”

       Jimmm tayi sannan ta rike kasan maranta tace Uncle nan gurin yana yawan min zafi “

    Karki damu yana neman wajen gyara zaman sa ne da kyau Dan kar ki takurashi”

      Wanene, Wai kaima da gaske gani kake ciki garan to ta Ina ??

    Dariya sosai Ahmad yayi itako Samha fadi take wlh Banda komai Kuma zaka gani ai”

     Kwanan Samha biyu da dawowa yanzun sau daya Ahmad ya nemeta ganin aman da taitayi bayan yasamu nutsuwa yashi barinta har cikin yayi kwari yayin da duk wannan irin wahala da takesha kowaye yace ciki gaemeta Bata taba yadda ba”

     Gaba gaba ciwo Samha karuwa yake yi, yayin da Ahmad ya tattaro hankalinsa gaba daya ya maida Kan Samha, aikin ya daina zuwa faba daya tare da kashe wayarsa”

     Gaba daya gidan nasu duk ya birkkce shi kanshi Ahmad din ya rame”

Tsaki taketaja yayin da Ahmad ke matsa mata jiki sinka sinka kwance take Kan cinyarsa tayi daisai”

    Wai tsakin me kike ne tun dazon??.

   Kanta tsaye tace Mamana”

   Bangane ba”

    Uncle nace Mata ta koma gidan Abba na taki”

     Wow yarinya me wayau, ki dage kicigaba da matsa Mata, wannan shawara ce mekyau”

    Toh Uncle ka Mata mgn mana”

   😳😳 Ke rufamin asirin Fatima yanzun bada bane kinsason in sake yin wani laifin ne wajenta, kedin ce dai Zaki dage Mata”

    Uncle cewa tayi fah Wai as aurenta zatayi”

    Kadan daga aikinta kenan”

      Jimmm tayi sannan tace Niko Uncle Ina tausayin Abbana da ace acan gidan nake wlh duk wadda yazo gurinta saina koreshi shi, koma wlh naso ace Ina da kani ko yaya dazan saka ya Kira min duk wadda zaizo gurinta”

   Ko yanzun ma kisa aranki kina dasu, idan kince In zama yaya ko kanin ki zan zama indai wannan ne baki da matsala…….

WATA FITSARA

     By
Fadeela Lamido

PAGE 35

Kwana biyu lafiya kuwa kake?, Ni sai Ina ganin ka wani iri”

    Bakomai Momy”

    Ai shikenan, ko zamanka gidan kaikadai zaisa ka cikin damuwa, nagaji da halinka ne Usman kacika bakar Zuciya, ka kasa zama da mace kamar jira kake ka wartaka yariya gidan su, yakwma ta kama kanka fada, yanzun zakaso asako maka Fatima….

   Ba zanso ba Hajjjah, shiyasa ma nayanke shawaran bazan Kara aure ba”

     😳😳 Haka zakaita zama?? Duka duka guda nawa kake??

    A’a Momy so nake Khadija ta dawo dakin ta”

    Murmushi momy tayi sannan tace”

      Ayau?, Sai yanzun ka tuna da Khadija?, Ba irin mgnr da ban makaba tuni akan ka dawo da ita ka rufe idonka narasa me Khadija tayi maka rana tsaka”

   Momy Kaddara ce kawai tarabamu ba wani abu ba”

    Toh yanzun Kun daidaita da Khadija ne???

     Zadai mu daidaita Momy, insha Allahu, kinsanta tacika kafewa cewa tayi wai bazata dawo ba”

    Hmmm ai zani ce ta tadda muje mu, duk ku biyun haka kuke zanfi kowa farin ciki idan Khadija ta dawo dakinta domin lokacin da kuna tare kafi kyaun gani tun bayan fitan Khadija duk kabar hankalin ka”

    Kawar dakai yayi cikin yanayin dake nuna yana cikin damuwa yace”

     Momy kitayani da addu’a, Khadija ta yadda ta dawo dakin ta”

    Itama cikin kawar dakaitace”

    Addu’a munanan munayi Allah ya zaba abun da yafi alheri”

        *********

Amai Samha ta gama kwarawa yayin da Ahmad yake tsaye akanta sai faman Sannun yake Mata”

     Uncle wai wannan wani irin ciwo ne nake yi ciwon yaki karewa kuma sai yawo ya dinga taruwa mun abaki”

     Sannu zaki samu sauki kinji”

    Ni uncle nagaji maganin ma da kake bani Kara min ciwon yake yi😫

     Kanta ya shafa Magani ai baya Kara ciwo Fatima ki Kara hakuri Zaki samu sauki”

     Nidai bazan Kara Shan maganin ba gaskiya”

   Hannunsa ya cire akanta sannan  ya zagaya bayanta ya zauna tare da sata atsakanin jinyoyin sa yarungume ta tare da sunbatan ta kigara hakuri nace ko Zaki samu sauki”

   Ni fa wlh Uncle nagaji😭

    Cikinta ya shafa, haba yariyata kefa jaruma ce, koda yaushi ki dinga nuna jaruntar ki saikiji jikin ki namiki kwari sosai”

     Ni vantabayi irin wannan ciwon ba narasa sunan shi”

   Acikin kunnenta ya tura bakin sa ingaya miki sunansa??

   Kaita daga”

  Sunan shi laulayi, kinsan laulayi?

    Lumshe idonta tayi Uncle da gaske ciki garan??

    Umm ciki gareki munkusa samun Yaro ko yariya”

   Jimmm tayi sannan tace gaskiya toh Uncle akwai wahala”

     Kizama jaruma saikiga abun yazo miki da sauki”

     Toh yanzun Uncle akwai mutum acikina?

   Zai dai zama mutum din nan gaba, yanzun kin yadda akwai ajiyana ajikin ki??

     Kaita daga sannan ta sake cewa, yanzun toh bakajin kunyan ace kamin ciki?? Karasa mgnr tayi cikin rufe Ido”

   Murmushi yayi sannan yace”

   Bude idonki, ni banajin kunyan kowa, kina ganin ko zanji kunyane ‘yata nada cikina ajikinta??

     Kirjinshi ta kwanta toh kaifa Babana ne Amman Kai ko ajikin ka”

   Shima kansa ya Kara mannawa ajikin ta ni banajin kunya, Hajiya kawai yanzun nake danjin nauyin ta kadan”

    Wacece Hajiya??

    Mamanki”

   🙄🙄 Hajiya Kuma?? to ai bataje Hajji ba??

    Umm ai basai taje ba, kawai sunan ne yake min nauyi”

   Hmmm dafa Khadija kake ce Mata?, to ai yanzun ma ba hajiya yakamata kace Mata ba Umma zakace yadda nake gaya Mata”

       🙄🙄 Kawar dakai yayi sannan yace”

  Nine zance Mata Umma nafa girmeta??

    Jimmm Samha tayi ajikin sa sannan tasa hannun ta ta tureshi”

  Kallo yabita dashi tare da fadin meya faru kuma??

   Hawaye yagani makare a idonta, kokarin mekewa take yace yaya akayi?

      Toh inba wulakanci ba saika dinga cewa ka girmeta😫😫

   Murmushi yayi au dan wannan kike fushi??, Shikenan ta girmeni nabar Mata wata uku ma”

    Harara ta zabga masa sannan ta wuce dakinta”

    Dariya yayi sosai sannan yabi bayanta”

  Kusa da ita ya kwanta, ahankali ya saka hannunsa cikin nata, Fatima nabari kinji, gaya min me kike so?

       Batare data kalleshiba tace kace Mata Umma”

      Toh naji an gama,  hannunsa ta ruko ta tura akirjinta, fahimtan inda ta dosa yasa ya fara wasa da ita sosai ta saki jikinta kamar ba itace mara lafiyar ba, sakewa sukayi da juna sosai cikin nishadi suka gamsar da junan su”

    Saidai suna rabuwa da juna tafara rawan sanyi, bargo yamata da jikinsa yana mutsuka hannunta yake fadin  kinga irinta ko”

   Sosai ta rugumeshi zafin jikinta yaita shiga cikin shi ahankali kan kace me zazaabi ya rufe shi, daker ya zame jikinsa ya dauko Mata magani sannan shima yasha magani me zakici??

     Ni koma menene Amman wadda Hajja ta girka”

   Toh fah, shikenan barije ingani”

     Misalin 4 na yamma ya isa gidan Hajjah bayan sun gaisa ta tambayeshi Samha”

   Alhamdulillah Hajjah Amman fa tanajin jiki Hajjah, yanzun ma cewa tayi abincin ki take so”

    Ton ai dama naso inzo gidan  naku Galadima yace baka zuwa aiki, me zai hana ka kawo Fatiman nan gidan domin kasamu ka dinga zuwa aikin ka”

   Jimmm yayi sannan yace”

   Gaskiya Hajja saidai inkawota idan zan tafi Office da Yamma Kuma inzo in dauketa”

     Meye dalilin hakan Ahmad?? Ita Kuma shikenan kullum tana hayan ga karamin ciki”

  Kawar da kansa yayi bece komai ba”

    Wani irin kallo Hajja tamai sannan tace”

   Bakace komai ba? Asibitin ku na bukatar ka, Kuma irin ciwon nan harsai yayi kwari tukun zata fara Jin dadi”

      Toh ai Hajjah ni gidan ne ni daya ba Dadi zaimin ba”

      Ikon Allah, Hajjah tafada, nandin bakon kane?, Toh ku tattaro mana kudawo nan din Kan tadanji dadi”

     Nan ma shiru ya sake yi tare da kawar da kansa, zuwa can yace shikenan”

      Sosai Hajjah ta fahimci baya so Amman dole haka din ne mafita, dan haka taki kallon yanayin fuskansa”

    Abincin ta hada masa ya dauka ya tafi”

           ***********

     Misalin 9 na dare wayar Samha tayi Kara”

   Ahmad ne ya daka ganin Abbanta ne yai saurin Mika Mata wayar”

     Cikin gimamawa ta gaidashi”

  Shima cikin fara’a yake amsawa”

       Abba bani da lafi fah bakazo ka ganni ba”

   Toh ai baki Gaya min ba Mamana, mijiki ma be Gaya min ba, meke damun ki??

     Laulayi nake Abba”

      Shakewa Alhaji Usman yayi Dan haka Saida yai gyaran Murya sannan yace sannu Allah yabaki lafiya, amman dai kinacin abinci dai ko?

      Eh Amman nafi son wadda Hajjah tayi”

     Toh sai kuma me kike so wadda zan iya kawo miki kici??

     Shiru tayi zuwa can tace Abba Ina naji inason wani abu zan Kira ka”

   Toh ba damuwa, Allah yai muku albarka, Mamanki tasan baki da lafiya??

   Eh tasani”

   Yayi kyau

   Ammm….. Abba na??

  Na’am Mamana?

    Har yanzun kaikadai ne agidan??

   Jimmm yayi sannan yace”

       Eh yaya aka yi?

       Bakomai Abba Amman dan Allah kayi aure Abba”

   Kin fara ko???

    Abba inma wata mgn bazaka min fada ba??

   Inajin ki??

    Dan Allah ka maida Mam…… Kasa karawa tayi tare da toshe bakinta Dan batasan inda zai dauki zancen ba”

      Inajin ki Fatima karasa mana bakomai”

   Abba so nake kadawo da Mamana”

   Lumshe ido yayi zuwa can ya bude, Mamana shiyasa nake son ki sosai, saboda kina damuwa da damuwata sosai, bakison kika na takura, tun kina ‘yar karamar ki, Kuma nasan rashin mahaifiyarki nai miki ciwo acikin ranki, haka nima rashin Khadija namin ciwo fiye da yadda yake miki ciwo saidai wani dalili ya hanani nunawa, tunanina akwai son wani azuciyarta dan haka na tilastawa kaina kin zama da ita wadda saidaga baya nafahimci wasu abubuwa, hankalina ya kwanta domin Ina tunanin zan Kuma samunta akaro na biyu wadda bazatan taba yadda abun da yafaru baya yasake faruwa ba Amman Kash, guiwata tayi sanyi lokacin danajewa Khadija da zancen komawarta”

   Fatima?, Naje gurinta da niyar in maidata dakin ta saidai Bata bani hadin kaiba tace ita Sam bazata dawo ba….

   Abba dan Allah kabata hakuri”

    Hmmm kidai tayani da addu’a Mamana Nima inason dawowanta fiye da tunanin ki”

    Abba in Mata mgn??

     Hmmm, kimata, abun da tace miki ki kirani ki gaya min”

    Dahaka suka aje wayar yayin da Ahmad duk yanajin amsoshin da take bawa Abbanta saidai koda yaga tagama wayar bece Mata komai ba itama batace masa komai ba har washegari

    Alhaji Usman bayan yagama waya da Samha wayar Khadija ya Kira, domin Samha ta sosa masa inda yake masa kaikayi”

    Beyi tunanin zata daukaba Amman abun Mamaki dauka tayi, sai dai batace komai ba ko sallama Babu”

   Khadija??

    Yaya akayi??

   Jimmm, yayi sannan yace”

  Inason inyi mgn dake”

   Ina jinka”

     Khadija kafin ki yanke min hukunci ki tuna irin soyayyar da mukayi abaya, sannan ki duba iya zaman da mukayi tare, nasan munji dadin juna, karki yanke min tsatauran hukunci akan  kuskurena guda daya wadda na aikata cikin zafin kishin ki”

       Usman?

   Na’am Khadija”

    Usman?

   Ina jinki Khadija”

    Kafita daga idona”

   Ki saurareni”

    Nagaya maka kafita daga harkata, bakasan darajata ba tunda nabar gidanka banzama tafini daraja, kwata kwata baka bani hakkina ba, katakura min karabani da ‘yata idan inason ganin ta sadai in bita makaranta Ina rabe rabe kamar Mara gaskiya, bayan Sakin wulakancin dakamin, Ashe wannan ba komai bane, baka tashi wulakantani ba Saida katashi auren da Samha katura min bakincin da yakusa zautar Dani, mafarkin yau daban na gobe daban, Usman sai yanzun da Allah ya taimakeni yaye min damuwa sannan zakazo min da wata banzan mgnr ka, Usman Saida ka kwance min zani atsakiyar kasuwa sannan yanzun kace zaka daura min,  Allah ya kauta”

     Duba Khadija, ki saurare ni, duk abun da kike son yanzun shi za’ayi, kibani daman in ganki, Ina tabbatar miki da cewa zan gyara kurakuren da nayi abaya, zan gyara su kuma zakiji dadi duk yadda kike so haka za’ayi insha Allahu zan wanke laifina, gobe zanzo na same ki, agida muyi mgn, duk laifukan da kika dafa na dauka”

********

Washegari Ahmad ya nufi gidan Hajjah da Samha, saidai be Gaya mata can zaibarta ba domin yana tunanin bazataji dadi ba jikin shi take kwana kullum wani irin shiga jikinsa takeyi, ya lura da ita sosai take son jikinsa”

     Har falon Hajjah yakaita sannan sannan ya mike yana fadin”

   Barinje Office indawo”

  Harya juya Samha tace, Uncle”

    Na’am

    Idan zaka dawo kabiya gidan Baba kacewa Mamana tabaka abun me dadi ka kawo min”

        A’a nikam bazan iya ba Fatima, zan nimi wani abun ahanya in sawo miki”

     Ni ai wadda tayi da kanta nake so”

    Kansa ya shafa tare da fadin shikenan ki kirata a waya ki gaya mata in naje sai  ince abani sako kawai”

     Toh kawai Samha tace badan tayi niyar Kiran ba”

     Itako Khadija yau da Shirin zuwa gidan Hajjah ta tashi dama sabo da Ahmad ne batacika son zuwa ba Amman yanzun tasan Ahmad baya gidan Kuma ko zasu hadu gaisuwa ce kawai dan haka can zataje tai zamanta kodan ta gujewa haduwa da Alhaji Usman……

    Cikin Fara’a Hajjah ta tare Khadija, bayan sun gaisa tace”

    Daga Ina kike da kaya”

   Daga gida nake Hajjah kawai nagaji da zama guri daya ne nace barin zo nan nakwana biyu”

   Masha Allah Alhamdulillah, gaskiya Khadija baki taba burgeni irin na yauba, aina dauka shikenan Kuma auren Ahmad ya lalata zumuncin ganin tsayon shekara guda baki tako gidan nan ba, aishi aure nufine na Allah Allah ya kadarta matarsa ce ba Yadda za’ayi, dake da Samha da Ahmad din ni duk nawane, mahaifinki yasha nono ya rage min, uwarmu daya ubanmu daya, kinga tushen mu daya gindin mu daya, dan Allah kada wannan ya lalata mana zumunci ayishi fiye da da”

     Nasiha sosai Hajjah tai Mata me shiga jiki bayan sundan taba hira ta nufi dakin Hajjah domin ajiye gayanta”

      Samha ta hanga tsakiyar gadon Hajjah sororo ta tsaya tana kallonta, cikin tsawa tace”

     Au nan Kuma kikayo”

   Juyowa tayi ganin Ummanta abun ya Bata Mamaki cikin sauri tace”

     Aishi ya kawo ni”

   Tsaki Khadija taja sannan ta aje kayanta ta fita aranta take fadin”

       Mijin tace yanzun haka ita tace ya kawo ta duk dai tsiya ai bazaku kwana dai ko?

     **************

Misalin 5 na yamma Ahmad ya dawo, ganin Khadija agidan abun yai matukar bashi Mamaki, dama yaje ance Bata nan, akan kujerar falon ya zauna tare da gaidata”

    Yauce kawai Khadija ta amsa masa gaisuwa kamar yadda ya dace”

     Sosai yaji sanyi hankalin sa ya Kara kwnciya”

Kanshi akasa yace”

    Ashe kina nan daga can nake akace baki nan”

     Eh Ina nan wani abu ne?

     Daman Fatima tace inzo in amso Mata Sako gunki”

    Cikin murmushi Hajjah tace ninama mance tace abincin ki take son ci”

     Tabdi lalai ni ai bana girgi
Girkawa ake abani

     Cikin Murmushi Hajjah tace wannan na musamman ne zaki girka naki ake so”

    Kawar da Kai Khadija tayi zuwa can ya rufe Ido”

       Ahmad kuwa kulewa yayi acikin ransa yake fadin”

    Har yanzun matar nan Bata Sona inda tana so jikinta na rawa zata dafawa Fatima abunda ranta ke so kamar yadda  Hajjah keyi”

   Mikewa yayi ya nufi dakin Hajjah ya dade aciki, Khadija na lura da Hajjah sai kallon Hanya take da alama tason ta shiga dakinta Amman shiru, Kiran Sallah mangariban da aka kwala yasa Khadija fadi acikin zuciyarta yanzun dole ya fito ai, saidai abun Mamaki har aka idar da Sallah Ahmad be fito ba ita da Hajjah nan sukayi Sallan su afalon”

      Abinci sukaci har suka gama babu Samha Babu Ahmad”

      Lallai Khadija keta fadi cikin zuciyarta yayin da take ganin kokarin Hajjah da ake Mata wannan fitsaran acikin gidan ta”

      Ana daf da Kiran isha’i  ya fito, cikin sauri ya bi tabayan kujerun ya shige gefen sa”

    Kusan minti 15 da shigansa ya fito da sauri cikin Jallabiya yana kokarin fita yana gyara hannunsa alamar cikin sauri aka sakata”

     Suma duk nan sukayi Sallan kamar dazon Hajjah ce ta fara shiga dakin”

  Itako Khadija Mamakin hali irin na Hajja take”

    Zuwa can ya mike ta shiga dakin adaidai lokacin da Hajja ke mikawa Samha kayan baccin ta”

    Amsa tayi ta Sanya sannan ta zauna tana yamutsa fuska gashin kanta jike da ruwa, hakanan ta zauna kujeran gaban madubi cikin yanayin nuna tana Jin ki”

    Haushi Samha kebawa Khadija sosai musamman yanzun da take kallon irin iskancin da sukeyi gaban Hajjah”

     Umma dan Allah ki gayara min gashi na”

   Cikin sauri Khadija ta dago idonta ta sauke shi ana Samha”

     Dan Ubanki Ina Wasa dake??, Ki shiga hankalin ki banson Iskanci fah”

    Da sauri Hajjah tace meye haka Khadija?, Dan tace ki taimaka Mata kike zaginta”

Karasawa tayi ta fara gyara Mata Kan nata, busar Mata dashi ta fara sannan ta shafe shi da mai hardasu turare, Hijjabi hahhaj ta zura Mata bayan ta Sanya Mata hula”

       Sallah tayi mangariba da isha’i sannan ta koma gado ta kwanta

   Bacci ne me Dadi ya dauketa yayin da hira ya sarke tsakanin Hajjah da Khadija, suna hiran tana kallon yadda Usman keta nacin kiranta yana nanatawa”

     Gajiya da ganin number tasa yasata jefa wayar cikin jaka yayin da sukaci gaba da hiransu da Hajjah”

      Shigowan Ahmad yasa Hajja saurin kallon agogo, sannu ya musu sannan ya karasa kusa da Hajjah ya zauna idon sa akan Fatima dake Bacci”

      Yadda yake kallon Samha har so yayi yabawa Hajjah kunya duk da cewa tana kyauda ido”

    Itako Khadija koda wasa Bata kalleshi ba”

    Daga can tajishi kasa kasa yanaiwa Hajjah mgn”

    Hajjah Wai Bacci take ne??

      Eh tunda tayi sallah take bacci”

   Shiru yayi saidai duk da haka idon sa na kanta, ahankali ya sake cewa”

    Hajjah dan tada min ita mutafi”

    Inace anan zaka barta?

     Eh Ina nufin muje part dina  mana”

    A’a Yaro kabarta tunda ta rikiga tayi bacci”

    Gaba daya diriricewa Khadija tayi domin koda yake mgnr kasa kasa tana Jin shi”

     Hajjjah dan Allah ki tada min ita muyi da ita acan zata kwana ai”

     Cikin kosawa Hajjah tace Kana iya tada ta ai”

        Kansa ya shafa sannan yace”

   Haba Hajjah  ki taimaka mana”

   Dauke kanta tayi yayin da yasata kallon gefen Khadija yai saurin shafa kansa tare da mikewa ya nufi kofar”

   Tausayi yabawa Hajja dan haka tace tsaya intada ka inzata toh in Bata zuwa babu me takura Mata”

    Hannunta tasa ta Dan daki Samha kadan tace umyim cikin yanayi irin na me bacci”

   Tsareta da ido Hajjah tayi tare da fadin”

     Wai zakibi Ahmad part din shi??

    Batare data bude idontaba tace yadawo ne??

       Eh gashi nan tsaye, bude idonta tayi ta kalleshi, murmushi ya sakarmata lokacin yabawa Khadija baya, bayansa kawai take iya gani yayin da ta hangi fuskan Samha cike da murmushi”

   Hannu ya mika Mata ta rike yayin da ya dagota ta fara kokarin sakkowa tare dasa hannunta ta zago dashi ta cikinsa, shikuwa kugunta ya zago da Hannun sa yayin da ya rankwafo da kansa yanai Mata mgn suka fice”

Hajjja fuskanta cike da murmushi take binsu da kwallo ba ita ta bariba Saida suka vacewa ganinta sannan ta shiga masu addu’a cikin zuciyarta”

      Khadija ko cikin ranta take fadin,

    Samha ma fitsarriya ce Ashe babu kunyar uwan mijin ko kadan attare da ita wannan wacce irin rayuwa ce, dubi inda ta makaleshi cinyoyi awaje zagada zagada Babu rigar kirki”

     Sosai taga Rashi dacewar abun acikin ranta tace bazan iya ganin wannan Fitsarar ba gobenan zan tafi gida”

        **********

  Washegari misalin 8:00am Ahmad ya fice Office lokacin Hajjah kadai ta tashi, misalin 10 Khadija ta tashi wanka tayi sannan ta fito falo tana karyawa, lokacin Samha fito gaida kowa tayi sannan ta zauna tana leka abun da Khadija keci”

   Hararanta tayi yayin Samha tai murmushi tare da fadin kinsan me zanci?

    Cikin sauri Khadija tace dawa kike??

    Nifa da Hajjah nake mgn”

    Hajjah kakarki ce??

    Kakarta ce ni mana, aini nafison hakan Khadija meyasa ke kin fiye fada”

     Juyawa tayi tacigaba dacin abincinta yayin da Hajjah ta juyawa gurin Samha Ina jinki me zakici”

      Wainar fulawa”

   Abu me sauki, barin je in soya miki”

     Hajjah ninafin inyi dakaina”

    Cikin Mamaki Hajjah tace toh barin je in hada miki komai”

   Hajjah kiyi zamanki zan iya, mikewa tayi ta nufi kitchen din yarin da fuskan Hajjah take cike da murmushi”

     Samha ma ciki da hanna shuwa tashiga kitchen din saidai tana tsakiyar kitchen din taji wani irin Santsi ya debeta zare ido tayi Jin tatafi luuuuhh ji kake timmmm😬

Wani razanan nan nen Kara data kwallara shiyai sanadin da Khadija da Hajjah suka nufi kitchen din afirgice”

    Khadija ce agaba ganin Samha kife akasa ko motsi batai yasata ko  tsayawa cak tare da dafe kirji, itako Hajjah fadi take innalillahi wa’innalaihir raju’un………

166 comments

  1. На форуме подсказали https://mfo-zaim.com/ , как хороший ресурс по микрофинансам. Убедила экспертиза — там работает Андрей Фролов, один из немногих, кто реально разбирается в теме. После его обзора я понял, где меня могли бы обмануть, и не попался.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *